Friday, July 29, 2011

KARIN AURE

Assalamu alaikum. A gurguje ina sanar da masu karatuna cewar Allah Ya azurta ni da karin aure ranar 16 ga Yuli 2011. Aurena na farko na yi shine ranar 6 ga Disamba 1998.
Na san akwai masu tambayar dalilin da yasa zan kara mata, menene dalili da sauransu to amma kasancewata Musulmi, Bahaushe ina ganin tsayawa nayi bayani kamar bata baki ne. A kullum abu ya samu mutum to mu kan danganta shi da kaddara duk da wasu zasu ce ai tilas sai mutum ya tanka. Haka ne.
Amma da farko a takaice dai ina zaton an fara maganar aure ne daga biyu ba daya ba. To ni ba malami ba ne, abin kawai da na sani shine Allah Ya bani kyauta kuma ina ganin ban isa na ce bana so ba. Ina matukar kaunar matata ta farko to amma tasowarmu a iyali da suka kasance mata a hade ban samu matsala ta azo a gani ba. Haka ina matukar kaunar amarya ta wacce ta nuna min kauna fiye da wata 'ya, kuma nayi kokarin ganin saka mata da abinda take kauna.
A duk lokacin da akayi karin aure addu'ar ita ce Allah Ya bada zama lafiya, Ya hada kansu, shi kuma mijin Allah Ya bashi ikon yin adalci. Don haka nake rokon addu'a daga kowa da kowa.
Na gode.