Tuesday, August 5, 2008

Hafsah


Sharhi kan Fim din Hafsah

Cast
Ali Nuhu
Zainab Idris
Nura Husaini
Hawwa Ali Dodo
Tanimu Akawu

Story development
Ian Masters
Sani Mu’azu
Iliyasu kasimu
Iliyasu Ibrahim

Script Consultant
Ian Masters

Research
Chinwe Nnoham

Camera
Ishaya Garau
Ibrahim Achimota

Editor
Babakarami Jos

Music
Habeeb M.
Nazeefi

Playback singers
Murja M. Baba
Nasiru idi
Habbeb M.

Production Executives
Jonathan Curling
Sani Mu’azu

Producer/Director
Sani Mu’azu

Sponsors
Lenscope Media
BBC World Service Trust.

Location
Bauchi

Gabatarwa
A kwanakin baya ne Hukumar tace finafinai ta Jihar Kano karkashin jagorancin Mal. Abubakar rabo da haramta sayar da kaset din hafsah a fadin jihar domin a cewarsu Hukumar bata wanke shi ba. A dalilin haka shi kuma shugaban MOPPAN kuma mai fim din Hafsah Mal. Sani Mu’azu ya garzaya kotu domin kalubalantar wannan matsayi na Hukumar. A hirar da akayi da Mal. Mua’zu a jaridar Daily Trust ta ranar 15 ga watan Maris 2008, ya nuna ai tunda an wanke fim din sa a Abuja baya bukatar wata Jiha ta wanke shi. Sannan shi kansa Mal. Rabo ya yabi fim din a wani shiri na gidan rediyo, inji Mal. Mu’azu amma daga baya aka haramta fim ba.
Haka kuma ana cikin wannan sai ga wasu takardu da aka raba a masallatan Juma’a a birin Kano sun bayyana rashin jin dadinsu da irin wadannan finafinai ciki harda Fim din Sister da Hafsah wadanda babu komai a cikinsu sai bata tarbiyya. Wannan takarda dai mai taken “Asirinku ya tonu ‘Yan Kwagilar yahudawa” ta fito ne daga wata kungiya mai suna Islamic Values Protection Forum (I.V.P.F.) (Kungiyar Bada Kariya Ga Tarbiyar Musulunci).
A takaice wannan fim na Hafsah ya tayar da kura a lokacin da Hukuma ke kokarin tsarkake harkar finafinai musamman a Jihar kano. To amma me fim din ya kunsa? Shin su masu daukar nauyin sa sun yi domin fadakarwa ne ko kuma domin watsa tarbiyyar ‘ya’yan Musulmi Hausawa aka yi shi kamar yadda waccan kungiya tace?

Labari
Hafsah (Zainab Idris) wata yarinya ce wadda a farkon wannan fim aka nuno ta na cin gudu biye da ita wadansu samari ne wadanda sunyi kama da ‘yan daba. A gefen titi ta ci karo da wasu rumfuna na yayin kara inda ta fada daya daga ciki kamar ranta zai fita ba tare da sun ga inda ta shiga ba. Ashe wadannan rumfuna na wadansu mata ne, musakai da suke fita yawon bara. Don haka ta zauna a wurinsu duk da matsayinsu. Ta tashi daga barci sai taji suna wakar barar da suke yi idan sun fita don haka ita ma ta rinka bin wakar. Su da kansu abin ya burge su saboda zakin muryarta. Dalilin haka suka fara fita da ita yawon bara a kan tituna.
A bangare daya kuwa wasu matasa ne masu sana’ar kade-kade musamman tallace-tallace ga kamfanoni da bankuna suke cikin tsakar gwajin wakokin karkashin jagorancin Faisal (Ali Nuhu) da Linda (Hauwa Ali Dodo). Sun shiga tsaka mai wuya saboda rashin samun jigo da muryar da ta dace domin burge mabukatan wake-waken. Har ta kai ubangidansu (Tanimu Akawo) ya fara gajiya da rashin ci gaban da suke samu don haka ya basu lokaci ko su gyara ko kuma su san inda dare yayi musu.
Faisal da ‘yan tawagarsa sun fara neman mafita, don komai ya tsaya cik. Sun fara tunanin hanyar da zasu kama. Suna cikin wannan hali kwatsam sai Faisal da Linda suka ci karo da su Hafsah suna bara a kan titi, don haka Faisal ya fadawa Linda cewar waccan muryar tana da dadi. Suka kira su Hafsah suka basu sadakar N500. daga baya suka bi sawunsu suka nemi cewar idan suka yi amfani da muryar Hafsah zata iya zama wata tauraruwa. Kande da Hafsah basu yarda da binsu ba. Duk da haka faisal ya bata katinsa mai dauke da adireshinsa ko da zata nemi wani taimako.
Suna barin wurinsu Hafsah sai ga gungun ‘yan dabar nan karkashin jagorancin Jangwada (Nura Hussaini) sun dira a makwancin su Kande inda suka bankawa rumfunansu wuta. Lokacin da wutar da kusa cinye kayan rumfunan sai Hafsah ta tuna da katin da faisal ya bata ko da zata bukaci taimako. Nan da nan ta tono katin. Ta nemi waya ta buga masa. Ya zo ya same su ruwan sama yana faman dukansu. A haka ya nema musu matsuguni. Ita kuma ya kaita wurin da suke gwajin wakokinsu. Nan ya bukace tada ta rera irin wakar da suke yi idan sunje yawon bara. Ta rera wakar wacce ta baiwa duk ‘yan kungiyar su faisal sha’awa saboda zakin muryarta.
Linda ta je ta nuna mata daki mai kyau a matsayin wurin da zata zauna. Linda ta fara tambayarta inda ta fito, to amma Hafsah ta nuna wani irin rashin jin dadi. Ana haka sai ga Faisal da wasu kaya da ya sayo mata, amma Linda tayi kyashin wannan kaya. Bisa yarda da Faisal yayi na biyawa su Kande kudin haya, Hafsah ta yarda zata sanya kayan.
Bayan ta shiga wurin wakarsu suna gwaji sai ta ji rashin dadin irin salon wakar da suke yi don haka ta bukaci ayi wakar gargajiya. Faisal ya fada mata cewar su basa wakokin gargajiya. Kawai sai ta kaure da wata waka ta gargajiya mai suna Jalla-ku-jalla inda hakan ya burge kowa a wurin.
Sun kai wasu Kande ziyara. Faisal ya nemi jin asalinta domin bata yi kama da suba. Ta nemi kawai yayi shiru. Sun koma wajen wake-wakensu don koya mata rawar zamani ita kuma ta nuna ita fa ba zata iya ba. Linda ta dan nuna mata irin rawar da suke so. Ta dai nuna ita ba zata iya ba. Linda ta furta cewar dama ita Hafsah ‘yar kauye ce, don haka ba zata iya komai ba. Ai kuwa nan Hafsah ta zuciya, ta tambayi makadin ko yayi zaman kauye, ya amsa cewar eh. Ta ce to ya buga mata kidan kalangu. Nan ta tsuge da wata irin rawa mai ban sha’awa. Abin ya ba kowa sha’awa a wurin. Tana cikin rawar sai ga ubangidan su faisal (Tanimu Akawu) a tsaye da wasu ‘yan sanda. Ya ce ai ba don abinda ya taras ba da yau zai sallamesu. Don haka ya bukaci ‘yan sandan da su koma.
A dalilin ganin irin soyayya da take neman shiga tsakanin Hafsah da faisal, Linda ta fara nuna kishi.
Anan cikin gwajin waka sai ga wani ya shigo cewar ga wata kuturwa tana neman Hafsah. Linda ta bayyana cewar bai kamata a rinka yawan zuwa kiran Hafsah ba balle kuma kutare. Faisal ya bukaci Hafsah ta dakatar da zuwa wurinta da su ke yi. Nan ta fara tattare kayanta saboda rashin jin dadin abinda ke faruwa. Dole Faisal ya hakura.
Wani lokaci Hafsah ta je domin ganin Kande wacce bata da lafiya har Linda ta bita. Linda ta samu daya daga cikin abokan zaman Kande har ta jiyo sirrin Hafsah. Sakamakon haka har aka nuno Linda ta ziyarci Jangwada.
Ana haka har faisal ya sayo wa Hafsah abin wuya mai kyau amma tace ita bata bukata domin akwai abinda ke damunta.
Bayan nan ta samu su faisal ta nemi izinin fita kamar yadda ta saba. Sun nuna mata su fa sun gaji da yawan fitar ta domin yana shafar sana’arsu.
Tafiya tayi tafiya, soyayyar Hafsah ta shiga zuciyar Faisal. Ya nuna mata shi bai taba ganin mace irinta ba. Amma ta dakatar da shi cewar ita ba son wata hulda da wani namiji, kawai dai suyi huldarsu ta waka.
Ita kuma Linda ta fara janyo Hafsah a jiki don jin wasu abubuwa inda Hafsah ta nuna mata ta daina shiga harkokinta. Nan Linda ta ci mata mutunci, ta kuma fada mata sai ta fallasa ta.
Saboda shiga halin kaka-ni-kayi da faisal yayi, ya shiga wani hali, hankalinsa ya dugunzuma, ya ware a cikin dakin kade-kadensu yayi ta tikar rawa. Yaransa suka zo suka zuba masa ido. A karshe sauran kiris ya fadi, Hafsah ta je a guje domin tallafarsa amma ya ce kawai ta kyale shi domin ita maciyiyar amana ce. Anan tace ita su fita daga harkarta. Nan tayi fushi ta kama hanyar fita daga wurin sai ga Ubangidansu ya dawo da ita inda ya nuna ai ita ce ta ceto su a wannan sana’a. Ya nemi a bata hakuri kan ci mata mutuncin da akayi. Tilas Faisal ya bata hakuri. To amma nan Linda ta fizgo abin magana ta kwalla kiran Jangwada. Nan ya fito da ihun yau karyar warai-warai ta kare. Ya fadi cewar Hafsah matarsa ce bai kuma turo ta don tayi rawa da waka ba. A dalilin haka ubangidan nasu ya bukaci Faisal daya binciko abinda yake faruwa domin shi fa ya gaji da wannan wasan kwaikwayo da ke faruwa.
Anan Hafsah ta nemi Jangwada ya sauwake mata. Nan ya bukaci naira dubu ashirin idan tana son ya sake ta. Ta yarda to amma ya ja kunnenta da na Faisal in ba haka ba zai tona wani asiri nata. Bayan nan Linda ta fallasa cewar ai Hafsah tana dauke da cutar kanjamau. Take faisal yace Linda ta bar wurin kada ta kara dawowa. Ita kuma ta fada masa cikin fushi cewar da ta zauna da mai cutar kanjamau gara tirela ta buge ta. Nan Jangawade yace shi dama Faisal bai san abinda ke faruwa ba?
Faisal ya tambayi Hafsah ko da gaske ne ta da wannan cutar. Ta fusata tace eh tana da ita kuma tana da aure, sai me?
Allah Ya yi wa Kande rasuwa. Hafsah tayi juyayin rasuwar Kande wacce ta rike ta a cikin wannan mawuyacin hali.
Faisal ya tambayeta abinda take shirin yi, tace ita Lagos zata koma. Yake fada mata shi ya rasa kanta musamman kan wannan cuta ta ta. Ta fada masa cewar tana nan a Hafsar daya santa kuma tana da kanjamau. Ya nace kan ta fada masa tarihinta.
Ta fara bayyana yadda ta hadu da Jangwada wanda wani matashi ne mai farin jini a kauyensu, ga shi a lokacin yana da irin mashi wanda yake wasa da shi a kauyen, har a kan kewayeshi ana kallo. Wata rana ya je gidansu Hafsah yace yana sonta. Ya kuma kawo maganar aure ita kuma ta yarda.
Bayan sun yi aure sun koma birni da zama. A haka ta samu juna biyu. Saboda laulayin cikin ta nemi zuwa asibiti, amma surukarta ta rinka bata maganin gargajiya maimakon zuwa asibitin.
A nasa bangaren, Jangwada ya rinka fama da wani matsanancin zazzabi. Shi ma dai ya rinka shan maganin gargajiya har ma wani lokaci ya kan sami sauki.
Ita kuma Hafsah ta shiga nauyayyiyar nakuda wacce ta sha wahala. Tilas dai aka kaita asibiti amma a dalilin wahalar da ta sha har aka rasa abinda ta haifa. A cikin irin gwaje-gwajen da aka yi wa hafsah a asibitin har aka yi rashin sa’a aka sameta da cutar kanjamau.
A haka fa kowa ya tsangwameta wanda hakan ya tilasta mata komawa cikin birni. To amma Jangwada ya hana ta sakat don kuwa yayi ta turo mata ‘yan banga don cuzguna mata. Dalilin haka ta samu su Kande wadda ta rike ta. A nan ta gane cewar matsalarsu iri daya ce domin su ma an tsangwame su saboda cutar kuturta.
Ta samu ilimi daga likitar da ke kula da ita kan yadda zata iya tafiyar da rayuwarta cikin kwanciyar hankali. Aka dora ta akan magunguna wanda wannan ne dalilin yawan neman izinin da take yi daga wurin su Faisal.
Faisal yayi mamakin labarinta don haka ya nuna cewar lallai tana da bukatar kulawa. Ya fada mata cewar matsalar sa shine ya guji ‘yan uwansa ne saboda ya samu ci gaba a sana’arsa ta wake-wake. To amma har yanzu yana kewarsu. Ta ba shi shawarar ya je ya sasanta da iyayensa da ‘yan uwansa. To amma sai mamaki ya kamata domin ga shi tana bashi shawara amma ai ita ma babu daidaito a tsakaninta da danginta. Sai ya nuna mata ai su suka guje ta. Shine ta nuna ba laifinsu ba ne, a’a jahilcin sanin cutar kanjamau ne ya kawo haka.
A bisa shawarwarin da suka yi, Hafsah ta je gida domin samun daidaito da dangin nata. Mahaifiyarta tayi mamakin ganinta. Ta kuma fadawa Hafsah cewar ai Jangwada ya lalace, ya bushe. A dalilin haka Hafsah ta ziyarce shi amma mahaifiyarsa ta kama zaginta cewar ta zo don karasa shi bayan ita ta saka masa cutar kanjamau. Nan ya nuna ai ba laifinta ba ne, laifinsa ne. Hafsah tace ya zai ce laifinsa ne?
Nan ya nemi gafararta domin halin da suka shiga shi ya janyo domin shi ya dauko cutar a cikin harkokinsa da yake yi da matan banza a birni. To amma tunanin babu cutar da bata da magani ya sa ya sakankance ya hau shan maganin gargajiya. Ya dai bata hakuri kan lalata rayuwarta. Ya kuma yi nadamar shiga wannan hali, ya fada mata cewar dalilin kai mata farmaki shine domin bakin cikin halin da suka shiga. Ta dai yafe masa amma ta bashi shawarar ya rinka shan magani, ta kuma karfafa masa gwiwar ci gaba da rayuwa.
Anan ya fada mata tarihin yadda ya sameta kafin suyi aure. Domin wata rana yaji muryarta tana waka yayi sha’awar muryarta ta wadda hakan ya sa ya je neman aurenta. Ya kuma bayyana mata cewar kudin daya bukata daga gareta yayi ne don sayen maganin da zai sha.
A karshe dai ya bayyana cewar ya sake ta. Mahaifiyarsa ta nuna ai tunda Hafsah ta nemi su sasanta ai ya kamata ya hakura. Ya dai tsaya a wannan matsayi nasa.
Faisal ya nuna damuwarsa kan dalilin nacewar da Hafsah tayi wa Jangwada. Tace ai ita don tana son taimaka masa ne. Nan faisal ya fada mata cewar shi fa son ta yake yi. Shin akwai yiwuwar su iya aure a tsakaninsu, a matsayinsa na wanda bashi da wannan cuta? Domin hakan na damun mutane da yawa. Take fada masa cewar a asibiti an taba fada mata cewar za’a iya yin aure da mai cutar da maras ita har ma su haihu ba tare da dan da zasu Haifa ya kamu da cutar ba. Ya ce to shi ko zai so yaje asibitin domin karin bayani don har ila yau ya san matsayinsa. Ta ce ta yarda amma tana son ta taimakawa Jangwada.
Hafsah dai ta zama kasaitacciyar mawakiya inda take wakar ‘HIV ba zai kashen ba’ inda take bayyana halin da ta shiga da kuma tabbacin rayuwa da cutar cikin kwanciyar hakali. Itama Linda ta shiga wakar tana karfafawa hafsah cewar kada ta damu.
Shi kuma faisal a wani baiti cikin wakar da sigar wakar rap yake cewar:
‘Just imagine how you’ll feel, if you are down and helpless and still got discriminated by your very own, read between the lines, it ain’t easy surviving through the rough, tough times, Hafsah the extraordinary how ever though situations, you never gave up, kept holding on, still keeping your head up, how many more can survive all you’ve been through. The cloudy days are over now. The sun is shining, yes, I’m signing out. I know your story gonna inspire a lot.’
Can kuma wata muryar a cikin wakar ta ke cewar:
‘despite your status you could still give hope to the hopeless. Hafsah lets keep hope alive’.
Wakar ta ba duk ‘yan kallonsu sha’awa ciki har da Jangwada wanda ya sara mata.
Nan fim din ya k are.

Darasi
Babban darasin wannan fim na Hafsah shine nuna rashin wariya ko kyamatar mutane wadanda suke dauke da wata cuta misali kanjamau da kuturta.
Amfanin fahimtar kasancewar wasu cututtuka.
Amfanin dogaro da kai.

Sharhi
Wannan fim yana shan suka musamman ga wadanda suke da kishin al’adar bahaushe da addinin Musulunci. Ina ganin masu fim dim ba su yi la’akari da ko daya daga bangaren addini ko al’ada ba illa dai kaunar kidan gargajiya da Hafsah take da shi.
Idan aka dauke rayuwar mutanen kauyen su Hafsah da kuma abokan zamanta a lokacin da su jangwada suka biyo ta babu inda aka nuna akwai wata al’ada ta Bahaushe ko kuma aka baiwa suturar bahaushe muhimmanci. Watakila za’a iya basu uzurin fim ne na matasa kuma musamman mawaka domin gaba daya a kananan kaya suke. Gajeruwan wanduna da guntayen riguna da duguzuzun suma ga samarin fim din da kuma matsattsun kaya ga matan musamman Linda wacce dama ita da alama ba Bahaushiya ko Musulma b ace a fim din ya nuna halin matasa na yau. Linda tafi Hafsah shigar rashin mutunci domin babu a inda aka nuno ta da shiga ta kamala. Ina jin wannan shine dalilin dirar mikiya da yawancin masu kallo suke yi ga fim din. Amma ita Hafsah kam da dan dama-dama tun da ta shiga wasu halaye da yanayin wurin ya kan sa ta canza ta sa doguwar siket.
Masu yin fim din sun dau sana’ar wake-wake ne kila saboda jan hankalin matasa kan sakon da suke son isarwa. Dukkan ‘yan kungiyar sun nuna burgewa wajen kwaikwayon yadda mawakan zamani su ke. Ta bangaren rawa lallai dukkan su sun cashe musamman irin rawar da Hafsah ta rinka takawa. Muryar da aka yi amfani da ita a wake-waken ta yi zaki kwarai, kuma su kansu wadanda suka bi wakar musamman Hafsah ta burge, kamar ita take rerawa.
Dole a jinjinawa Faisal (Ali Nuhu) bisa irin rawar da ya dinga takawa, da cashiya wacce ta nuna kowanne mataki aka bashi zai iya dauka a fim. Haka ita ma Linda (Hauwa Ali Dodo) wacce ta taka matakin fitowa a wani rol mai wahala, domin duk wanda ya taka shi tabbas zai gamu da fushin mutane da yawa. Uwa uba Hafsah ta yi kokari na fitowa a mai kanjamau, ga kuma zaman da tayi da kowanne fanni na rayuwa a fim din. Gata da kokarin son kidan al’ada kasancewar ta ‘yar kauye. Shi ma Jangwada (Nura) ya gwada irin basirar da Allah Ya bashi da iya zama komai ciki har da zama dan daba. Su ma kungiyar su Kande sun nuna irin yadda ake zama a wannan matsayi na musakai.
Labarin ya tafi daidai da jigon fim din duk kuwa da walankeluwa da aka rinka yi da hankalin masu kallo ta yadda da wuya a gane abinda zai faru a gaba. Kusan ganin yanayin jikin Jangwada babu wanda zai zaci za’a samu cutar kanjamau a jikinsa kila a nan ana son nuna wani sakon da masu irin wannan fim kan nuna na cewar ba’a gane mai cutar kanjamau ta fuska.
Jigon fim din ya dace domin kara wayar da kan jama’a tattare da kyamar wani jinsi na mutane. Ya kuma fadakar game da yadda matasa ya kamata su rinka hulda idan sun fita neman kudi musamman a birane. Ya nuna cewar za’a iya rayuwa ko da an kamu da wannan cuta, kuma kalmomin da aka ambata a cikin wakar karshe mai cewar ‘despite your status you could still give hope to the hopeless. Hafsah lets keep hope alive’ ta karfafa gwiwa kan kowanne matsayi da Allah Ya sa mutum.
Ai ba sai an fada ba, fim din ya dauku matuka, kyamar rangadadau. Location din da aka dau fim din a garin Bauchi ya burge saboda yanayi da kuma amfani da wurin gwajin kade-kaden. Jarumai sun bi umarnin darakta sau da kafa. Kana ya nishadantar da mai kallo, musamman matasa.

Matsaloli
Kamar yadda na fada a baya, babbar matsalar fim din Hafsah shine rashin baiwa al’ada ko addini muhimmanci.
Babu inda aka nuna Faisal ya je wurin mutanensa domin neman gafararsu.
Hafsah ta fadawa Faisal cewar za’a iya yin aure tsakanin mai dauke da cutar kanjamau da wanda bashi da ita, me yasa ba’a yi cikakken bayani ba domin kila hakan zai kara nuna kauna ko kaucewa tsana ga masu dauke da cutar.
Kayan da jangwada ya rinka sanyawa kamar ya dade yana sawa, misali tun yana kauye har kuma karshen fim din. Me ya faru?
Me yasa ba’a nuna yadda za’a guji kamuwa da cutar kanjamau ba? Domin babu wani darasi da zai nuna Jangwada ya shiga wani hali, kila ma a nuna ya mutu domin gudun kamuwa maimakon har azo kan tsangwamar mai dauke da ita illa dai yanayin daya shiga, mai kowacce irin cuta ma zai iya shiga.
Me yasa aka sanyawa sunan fim din Hafsah? Domin anyi kukan cewar sunan yana da girma a addinin Musulunci. Kamata yayi a sa suna kamar ‘Tsangwama’ ‘Fadakarwa’ ko makamancin haka.

No comments: