Monday, August 11, 2008

Sharhin Fim din Nakiyar Kan Kashi

NAKIYAR KAN KASHI
Kamfani - Al-Khalil Film Productions
Mai shiryawa - Ibrahim Khalil Dan-Shagamu
Umarni - Ahmad S. Alkanawiy
Masu Fadakarwa - Kabiru Maikaba, Umar Bankaura, Bashir Nayaya, Ibrahim Khalil, Hajara Usman, Ladi Mutu-Ka-Raba, Zainab Booth, Binta Mohd, Zainab Ibrahim Kanya, Ummi Ibrahim dss.

Labari
To yau dai a takaice zan bayar da yadda wannan fim yake. Khalil (Ibrahim Khalil) dai dan jarida ne wanda yake gabatar da wani shiri mai farin jini a gidan rediyo. A cikin irin masoyan wannan shiri nasa har da wata yarinya mai suna Zillaziya (Ummi Ibrahim). To soyayya dai ta shiga tsakaninsu kuma har yaje wajenta a gida don tattaunawa da ita kan yiwuwar aurensu.
Khalil ya fara cin karo da matsaloli guda biyu; mahaifinta dai Baba Iro (Bashir Nayaya) abin duniya ne kawai ya rufe masa ido; baya bukatar ganin wani a wurin ‘ya’yansa sai hamshakan masu kudi. A takaice ‘ya’yansa mata jari ne a gareshi; daya matsalar kuma ita ce Zillaziya tana cikin gungun wasu kawaye wadanda suma babu abinda ke gabansu illa su samu kudi ta kowane hali, kuma basa bukatar ganin tayi aure. Don haka wadannan bangarori biyu suna yin barazana ga son dake tsakanin Khalil wanda bai taba aure ba da da Zillaziya wacce take bazawara ce.
Kamar yadda aka san iyayenmu wajen hangen nesa, magabatan Khalil basu so wannan nema ba, musamman irin gaggawar saka auren cikin sati daya ba tare da cikakken bincike da natsuwa ba.
A takaice dai an yi aure. Khalil ya fara fuskantar matsala ta farko ranar da suka tare inda ta nuna masa ita fa tana cikin al’adarta ne. Sauran matsalolin da ta kawo masa sune:
Ba zata rika yin girki ba, sai dai a rika sayowa ko kuma a dauko ‘yar aiki.
Kada ya rika saka mata ido a cikin harkokinta da abokan huldarta maza da mata.
Bata son wa’azi da kuma fada.
To a dai wadannan matsaloli abubuwa suka yi zafi har dai akarshe aure ya mutu.

Fadakarwa
Wannan fim yazo da daya daga cikin matsalolin da suka addabi wannan al’umma. Fadakarwar da fim din yake koyarwa sun hada da:
Labarin yana da muhimmanci domin kaucewa zaben tumun dare.
Yana nuna cewar iyaye suna da babbar gudunmuwa wajen shawartar ‘ya’yansu musamman wajen harkokin neman aure.
Yana nuna irin rikon sakainar kashi da wadansu mata kan yiwa ‘ya’ya musamman mata da aka bar musu.
Yana nuna illar barin ‘ya’ya suyi kawance da wadansu ba tare da cikakken binciken irin kawayen da suke hulda da su.
Son zuciya na jawo rashin kwanciyar hankali.
Muhimmancin zaman aure, domin babu wata kwangila ga mace fiye da gidan miji.
Yana nuna cewar gaggawa musamman a aure aikin shaidan ce.
Uwa-uba, rashin bin shawarar iyaye, rashin natsuwa, rashin bincike duk kan haifar da auren dana-sani har mutum ya dauko nakiyar kan kashi.

Abubuwan Burgewa
Ya kamata a yabawa Ibrahim Khalil wajen zakulo irin matsalolin da suka dabaibaye al’ummarmu. Babbar matsala ce wacce tayi katutu; samari kan yi aure cikin gaggawa ba tare da kwakkwaran bincike ba; mata masu neman aji kan shiga halaka ta hanyar shiga harkoki marasa dadi; iyaye kan mayar da ‘ya’yansu mata haja don neman kudi dasu.
Wani abin kuma shine yadda aka kaucewa rawa da waka marasa amfani. Anyi kokari wajen saka wakoki masu fadakarwa a matakai daban daban da suka dace da yanayin da ake ciki a fim din.

Matsaloli
Kadan daga ckin ‘yan matsalolin wannan fim sune:
Mahaifin Zillaziya yana wuce gona da iri wajen bayyana kwadayinsa a fili ba tare da bi a hankali ba. Da wuya ace mutum mahaifi musamman Bahaushe, Bafillatani ko danginsa su rika yin irin yadda yake yi balo-balo duk da rashin abin hannunsa.
Zai yi wuya ace Khalil ya yarda ya ci gaba da neman Zillaziya musamman a tashin farko daya fara cin karo da matsaloli; ina ma ace ya samu wasu dalilai kwarara daga baya bayan soyayya ta kullu sosai sannan a taka masa burki.
Wani lokaci Khalil idan yana takarkarewa yana magana sai abin ya zama kamar na wasa wato ‘comedy’.
Bai kamata a ce Khalil ya barke da kuka ba duk da sharrin da surukinsa yayi masa. Namiji, dan book kuma wayayye bai kamaci ya barke da kuka don anyi masa irin sharrin da surukinsa yayi masa. Shima wannan kamar wasan ban dariya.
Duk da irin mugwayen halayen da gungun matan suke aikatawa ba a fayyace gaskiyar abin da suke aikatawa ba, sabanin yadda mai fim din ya fada kafin fitowar fim din a wata hira a gidan rediyo (Freedom) inda yake cewar su matan ‘yan madigo ne, amma sai gashi ta kasance kamar suna hulda da masu kudi ne maza a Abuja.
A bangaren Zillaziya, kawayenta, mahaifanta ba a nuna wata fadakarwa da zata zama ishara ga masu irin wadannan halaye ba. Ya kamata ace su ga wata illa da zata sa a kori gaba don mai kallo ya tabbatar cewar tabbas akwai illa wajen aikata hakan.
Khalil bai dau hukumci akan halayen matarsa ba;, ya dai yanke hukumci ne kan dalilin halayen da mahaifinta yake nuna masa kawai. Ya kamata yaga zahirin abubuwan da take aikatawa domin ya guji mai hali irin nata har kuma yayi amfani da filin da yake gabatarwa a rediyo domin fadakar da sauran jama’a domin bin iyaye, bincike domin gudun fadawa tarkon da-na-sani.

No comments: