Tuesday, August 5, 2008

Sharhin KUDI NE!


Sunan Fim: KUDI ne!
Kamfani:R.K. Studio
Labari, Shiryawa, Tsarawa, da Umarni: DanAzumi Baba
Masu Fadakarwa: Usaini Sule Koki, Bashir Nayaya, Shehu Hassan Kano, Ahmad S. Nuhu, Abba El-Mustapha, Amina Garba, Hajara Usman, Saratu Gidado, Zuwaira Abdulsalam da Zainab Idris.

JIGO
Kudi kare Magana

LABARI
Fim din ya fara ne da nuno wadansu iyalai guda biyu wadanda basa jituwa da junansu, basa ga maciji. Wadannan mutane sune Sinu (Shehu Hassan) da matarsa Adama (Hajara Usman) a bangare daya sannan da Danjuma (Bashir Nayaya) da matarsa Asabe (Saratu Gidado).
Suna zaune ne a gidan wani attajiri Alhaji Siddiku (Usaini Sule) inda suke yin aikatau a gidansa. To amma kasancewar wannan rashin fahimtar da ke tsakaninsu ya sa Alhaji ya fara gajiya da sasantawa, don haka a karshe ya yanke hukuncin basu jari na Naira dubu Dari Biyar-Biyar su duka biyun don hada su da abinda zai raba zaman da suke wuri daya har yake zama fitina.
To amma duk da haka kusan bata sake zani ba domin Danjuma musamman bai hakura ba. Haka su ma matan.
Ana haka har dai iyali suka samu kuma kamar yadda aka saba gani shi Sinu ya samu ‘ya mace wato Wasila (Zainab Idris) shi kuma Danjuma ya samu Mustapha (Ahmad S. Nuhu). Aka shiga soyayya ba tare da sanin hadin da ke tsakanin iyayen nasu ba. Rannan Mustapha yaje zance wurin Wasila, Sinu ya tambaye shi mahaifansa, shi kuma ya fada masa cewar shi dan Alhaji Danjuma ne. Nan take ya gaya masa kada ya sake zuwa wurin ‘yarsa. To haka shima bayan ya fadawa mahaifansa suka yi fatali da maganar.
Wannan soyayya mai sarkakiya ta janyo kace-nace tsakanin gidaje biyun. Amma su yaran tuntuni sun tsunduma cikin kogin soyayyar dasuke ganin iyayensu ba zasu iya raba su ba. Iyayen dai sun raba su amma a banza.
Wasila dai ta fice ta bar gidansu kan raba ta da masoyinta.
Kashegari itama Maijidda (Zuwaira Abdulsalam) wacce take gidan Alhaji ta tsunduma cikin soyayya da Balarabe (Abba El-Mustapha) wato dan shi Alhajin (Usaini) inda itama wannan soyayya ta gamu da nakasu daga Hajiya Sadiya wato mahaifiyar shi Balarabe. Dalilinta shine shi an haife shi cikin kudi don haka ya wuce matsayinta. A wannan dalili Maijidda ta arce daga gidan inda ta bar masa takarda tare da kaset na sako mai ratsa jiki, na bayanin cewar bata san ita ba ‘yar gidan bace don haka yanzu ta fice kuma bata san inda zata ba.
Alhaji dai yayiwa Hajiya nasiha da ta daina raina mutane marasa shi domin a sanadiyar takurawa Maijidda da tayi har ta bar gidan, hakan yayi sanadiyar kade ta da mota da yayi yayin binta don dawo da ita. To wannan nasiha dai da shige ta sosai.
A daya bangaren dai rigima ta ci gaba da rincabewa tsakanin Alh. Sinu da Alhaji Danjuma inda har Alhaji ya kirawo su don sasantawa da kuma jan kunnensu kan alfahari da dukiya da suke yi. Ya nuna cewar ai ‘ya’yansu sun fi su sanin abinda ya kamata amma su sun dage da kara habaka gabarsu don haka ya nemi su shirya amma suka ki. Anan dai ya basu sati daya na su dawo masa da dukiyarsa tunda sun ki natsuwa kuma sun ki yarda da hada ‘ya’yansu aure. Jin maganar kudi tasa suka shiga taitayinsu inda a nan take suka natsu kuma suka sasanta.
An yarda da batun auren shi kuma Alhaji yace idan har bayan sati ba a yi auren ba to fa zasu dawo masa da kudinsa.
Kudi kare Magana. Tilas suka hakura.
Wannan shine labarin wannan fim na KUDI ne!

SHARHI
Kamar yadda aka san Danazumi Baba wajen kawo sababin salo haka a wannan fim ma ya kokarta duk da kudi kan sa mutum ya kaucewa wani matsayi nasa, kamar yadda kudi yasa makiya a wannan fim suka shirya.
Labari ne wanda ya nuna yadda za’a iya canzawa duk mai wani mummunan hali akalarsa ta amfani da kudi wanda Hausawa kan yi wa take da kare Magana.
Umarni, labari , hadin ma’aurata sauti da daukar hoto duk sunyi kyau.


SAKO
Fim din KUDI ne! yayi kokarin gyara wadansu dabi’u da halayyar mutane da kawo sako kamar haka:
Amfanin kwantar da kai maimaikon tinkaho da masu kudi kanyi musamman ga marasa shi.
Nuna cewar kudi ba sune mutunci ba.
Kudi ba hauka ba ne.
Ladabtar da musamman matasa kan wadansu wasannin misali wasan mace da namiji.
Amfani da kudi wajen gyaruwar wasu al’amura maimakon amfani dasu don lalata mutane.
Amfanin nasiha domin daidaita mu’amalar mutane.

MATSALOLI
Ko da yake na san cewar KUDI ne! suke haifar da kaucewa nuna al’adar Bahaushe a finafinan Hausa to amma ya kamata a rinka kwatanta wakilcin tsarin rayuwa ta Bahaushe. Akwai wakoki a wannan fim. Nasan zai yi wahala a rabu da rawa da waka a finafinan Hausa ko kuma za a dau lokaci to amma ya kamata a dinga canza abin ta dabara maimakon kwafowa gaba daya.
Wakar farko ta Kudi tana da ma’ana, amma yadda masu nishadantarwar suka yi shigarsu, akwai ‘yar matsala domin ba kayan turawa ne kawai ke nuna kudi ba.
Waka ta biyu kam ba don harshen Karin wakar da Hausa aka yi ba gaskiya da sai mutum yace fim din Indiya yake kallo. Kai su kansu Indiyawa idan suka gani zasu yi farin cikin samun magada a wata nahiya.
Ya kamata a rinka kula da wani abu. A duk lokacin da aka haifi jarumi ko jaruma a finafinan Hausa to shike nan iyayen su sun daina haihuwa. Ya kamata a rinka dan jona ‘ya’ya mana. Ai akwai bambanci tsakaninmu da wadansu kabilun.

1 comment:

Fagge said...

A gaskiya wannan sharhi yayi matukar kyau domin ya nuna abubuwan da fim din ya nuna. Wannan mai sharhi yayi kokari ta kallon fim din acikin tsanaki. Dama nima ina da wannan lokacin danayi farin ciki. Da kyau.